Image source: Channelstv.com
Kungiyar Kirista ta Najeriya CAN reshen Arewacin kasar ta ce a shekarar da ta gabata kadai an yi garkuwa da mambobin kungiyar fiye da 500.
Sakatare Janar na kungiyar reshen arewacin Najeriya, Reverend Joseph Hyap ya ce suna da dukkan shaidun da suke nuna wannan adadi na mambobinta da aka yi garkuwa da su.
Hyap ya kara da cewa "ita da kanta gwamnatin jihar Kano ta ce an yi garkuwa da sama da mutum 2000 a shekarar da ta wuce, don haka idan muka ce an sace namu mambobin sama da 500 ba mu yi karya ba."
Ya ce ya tara fastoci 1500 da ya zauna da su domin tattara bayanan mutanen da aka sace da wadanda aka kashe ta haka ne suka gano wadanda lamarin ya rutsa da su, yana mai cewa an biya kudin fansa domin karbo wasu daga cikinsu, wasu kuma babu labarinsu.
"Ko a makon da ya wuce an sace wani fasto da sakatarensa da wasu mambobi, an sako uku daga ciki amma sauran har yau babu amo babu labari," in ji Hya.
Tuni dai gwamnatin jihar Kaduna ta fito ta karyata ikirarin kungiyar.
Source: Bbc.co.uk/hausa